Makarantun da aka rufe sun hada da na firamare da na sakandare.
Galibin makarantun suna yankuna takwas ne a lardin arewa mai nisa inda 'yan Boko Haram ke tafka ta'asa.
Yawancin makarantun - kamar wadanda ke kauyen Kerawa - ana amfani da su ne a matsayin sansanonin 'yan gudun hijirar Najeriya wadanda suka tsallaka cikin Kamaru.
Hukumomi a Jamhuriyar Kamaru sun ce 'yan kungiyar Boko Haram sun kashe kimanin mutane 1,200 a kasar tun daga shekarar 2013.